Yanzu Yanzu: An sulhunta Ali Nuhu da Adam Zango

Yanzu Yanzu: An sulhunta Ali Nuhu da Adam Zango

Rahotanni da ke zuwa mana sun nuna cewa an yi sulhu a tsakanin manyan fitattun jaruman nan na masana’antar shirya fina-finan Hausa, wato Ali Nuhu da Adam A. Zango a garin Kano, bayan gumurzun da suka tafka.

Hadakar kungiyar nan ta masu shirya fina-finan Hausa ta kasa wacce aka fi sani da MOPPAN karkashin jagorancin Abdullahi Maikano ce ta yi nasarar shirya jaruman biyu.

Anyi hakan ne a ofishin jigon Kannywood kuma shugaban majalisar amintattu na kungiyar, wato Malam Abdulkarim Mohammed a yau Asabar, 13 ga watan Afrilu.

Yanzu Yanzu: An sulhunta Ali Nuhu da Adam Zango
Yanzu Yanzu: An sulhunta Ali Nuhu da Adam Zango
Asali: Facebook

Sakataren kungiyar MOPPAN reshen jihar Kano, Malam Salisu Officer, ya tabbatar da hakan ga manema labarai, ya na mai cewa, yanzu Ali zai janye karar da ya kai Adamu a kotu.

A baya Legit.ng ta rahoto cewa, Ali Nuhu ya yi karar Adam A Zango a kotu kan cewa kotu ta shiga tsakaninsa da Zango kuma ya daina ba ta masa suna kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

KU KARANTA KUMA: Sakkawato: Birnin Shehu; inda yara kanana ke fita domin neman aikin yi

Wannan na dauke ne cikin takardan kirar kara wanda Ali Nuhu ya shigar a kotun USC da ke Fagge a Kano.

Kotun ta bukaci Adam Zango ya gurfana gaban a ranar 15 ga watan Maris na 2019 misalin karfe 8.30.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng