Kalli yadda Ministan Buhari ya gudanar da bikin zagayowar ranar haihuwarsa

Kalli yadda Ministan Buhari ya gudanar da bikin zagayowar ranar haihuwarsa

A ranar Laraba, 17 ga watan Afrilu ne ministan shari’a, kuma guda daga cikin jigogin gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari, Abubakar Malami zai cika shekaru hamsin da biyu a rayuwa, wanda hakan yasa ya shirya kwaryan kwaryan walima.

Legit.ng ta ruwaito an gudanar da wannan bikin murnar cikar Abubakar Malami shekaru 52 ne a gidansa dake babban birnin tarayya Abuja, wanda ya samu halartar gwamnan jahar Kebbi, Atiku Bagudu, da kuma wasu yan uwa da abokan arzikin ministan.

Kalli yadda Ministan Buhari ya gudanar da bikin zagayowar ranar haihuwarsa
Malami
Asali: UGC

KU KARANTA: Yan bindiga sun halaka mutane 18 tare da barnata dimbin dukiya a Katsina

Uwargidar Malami, Hajiya Fatima ta bayyana maigidanta a matsayin mutumin daya samu tarin nasara a rayuwarsa, kuma shugaba nagari wanda ya bayyana gogewarsa a harkar shugabanci tun bayan darewarsa mukamin minista.

Kalli yadda Ministan Buhari ya gudanar da bikin zagayowar ranar haihuwarsa
Malami
Asali: Facebook

Shi dai Malami an haifeshi ne a ranar 17 ga watan Afrilu na shekarar 1967 a Birnin Kebbi, kuma yayi karatun sharia a jami’ar Usmanu Danfodiyo dake jahar Sakkwato, bayan kammala karatunsa kuma ya fara aiki a kotun majistri a Kebbi.

A shekarar 2003 aka nadashi kwamitin sauraron korafi na zabukan kananan hukumomi a jahar Kebbi, sa’annan ya taba rike mukamin sakataren watsa labaru na kungiyar lauyoyi Musulmai daga shekarar 2002-2004.

Kalli yadda Ministan Buhari ya gudanar da bikin zagayowar ranar haihuwarsa
Malami
Asali: Facebook

Daga bisani Abubakar Malami ya koma jami’ar Usmanu Danfodiyo inda ya koyar a tsangayar ilimin sharia na dan wani lokaci, inda daga nan kuma ya koma ya zama lauya mai cin gashin kansa, a shekarar 2008 ya samu lambar girma ta SAN, a haka har ya zama jami’in shari’a na jam’iyyar CPC ta Baba Buhari.

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel