CP Mohammed Wakili 'Singham' ya nemi afuwar kungiyar NBA reshen Kano

CP Mohammed Wakili 'Singham' ya nemi afuwar kungiyar NBA reshen Kano

Rundunar 'yan sanda reshen Jihar Kano ya nemi afuwar Kungiyar Lauyoyi na Kasa, NBA, reshen Jihar Kano a kan zargin cin zarafi da hari da aka kaiwa wasu lauyoyi a jihar.

Kwamishinan 'yan sandan jihar Kano, Mr Wakili Muhammad ne ya nemi afuwar a yayin da ya kai ziyara hedkwatan NBA da ke Farm Centre a cikin birnin Kano.

Muhammad ya ce lauyoyi abokan tafiya ne hakan yasa ya dauki matakin neman afuwar kungiyar domin neman yafiyarsu da cigaba da aiki tare.

DUBA WANNAN: 'Yan kungiyar Boko haram sun shiga matsala: Wani hakimi ya tona musu asiri

Singham Wakili ya nemi afuwar NBA
Singham Wakili ya nemi afuwar NBA
Asali: Twitter

"Aiki na ba zai yiwu ba sai da lauyoyi, ina fatan za mu cigaba da aiki tare bisa yadda doka ta tanadar," inji shi.

Muhammad ya ce a shirye ya ke ya nemi afuwar kungiyar ta kowane hali da suke bukata; Ta hanyar rubuta wasika ko kuma ta kafar watsa labarai.

A bangarensa, shugaban kungiyar na jihar Kano, Musa Abdullahi Lawal ya mika godiyarsa ga Kwamishinan 'yan sandan bisa ziyarar da ya kai musu.

Ya ce kungiyar a shirye ta ke tayi aiki tare da 'yan sanda domin ganin an tabbatar da adalci.

A jiya (Laraba) ne NBA ta bawa rundunar 'yan sandan wa'addin sa'o'i 48 domin ta nemi afuwar kungiyar a kan cikin zarafin mambobinta da akayi yayin da suke gudanar da ayyukansu kamar yadda NAN ta ruwaito.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel