INEC ta bayyana cewar zaben gwamna a Sokoto bai kammalu ba

INEC ta bayyana cewar zaben gwamna a Sokoto bai kammalu ba

Hukumar zabe ta kasa mai zaman kan ta (INEC) ta bayyana zaben kujerar gwamna da aka yi ranar Asabar da ta gabata a jihar Sokoto a matsayin wanda bai kammalu ba.

Baturiyar zabe a jihar, Farfesa Fatima B. Mukhtar, ce ta bayyana da duku-dukun safiyar yau, Litinin, bisa hujjar cewar adadin kuri’un da aka soke ya fi adadin banbancin kuri’un da ke tsakanin ‘yan takarar biyu.

Kamar yadda sakamakon zaben na karshe ya nuna, jam’iyyar PDP ta samu nasara da adadin kuri’u 489,558 yayin da jam’iyyar APC ke biye ma ta da adadin kuri’u 486,145.

Ana fafata wa a matakin kujerar gwamna a jihar Sokoto tsakanin gwamna mai ci, Aminu Waziri Tambuwal na jam’iyyar PDP, da babban abokin hamayyar sa, Ahmad Aliyu na jam’iyyar APC.

75,403 ne adadin kuri’un da aka soke daga mazabu 136 da ke fadin kananan hukumomin jihar Sokoto 22, kamar yadda baturiyar zaben ta sanar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel