Idan kunne ya ji: Daga zuwa kwanan gida an tsini gawar wata budurwa a dakin saurayinta

Idan kunne ya ji: Daga zuwa kwanan gida an tsini gawar wata budurwa a dakin saurayinta

Wata babbar kotun majistri dake zamanta a unguwar Iyaganku cikin babban birnin jahar Oyo, Ibadan ta bada umarnin garkame wani mutumi mai suna Olaosebikan Sangodiji a gidan kurkukun Agodi bayan akan tuhumar kisan kai da ake yi masa.

An gurfanar da Sangodiji mai shekaru 44 gaban kotun majistri ne sakamakon tuhumar kisan kai da ake yi masa, inda ake zarginsa ya kashe budurwarsa mai suna Dupe Oluwole, yar shekara 26 a dakinsa dake unguwar Sangodiji, Asapopo cikin yanki Illaro na jahar Oyo.

Idan kunne ya ji: Daga zuwa kwanan gida an tsini gawar wata budurwa a dakin saurayinta
Idan kunne ya ji: Daga zuwa kwanan gida an tsini gawar wata budurwa a dakin saurayinta
Asali: UGC

KU KARANTA: Gobara ta lakume wani dan jariri mai watanni 3 a Duniya kacal a Kano

Majiyar Legit.ng ta ruwaito Dansanda mai shigar da kara, Sajan Segun Adegboye ya bayyana ma kotu cewa da misalin karfe 8 na safiyar ranar 12 ga watan Disambar shekarar 2018 ne Sangodiji ya murde wuyan budurwarsa, Dupe.

“Muna zargin wanda ake kara yana soyayya da mamaciyar ne, wanda hakan yasa ya gayyaceta zuwa dakinsa, amma tashin da aka yi washe gari sai aka tsinci gawarta a gidansa. Hakan ya saba ma sashi na 316 na kundin hukunta manyan laifuka na jahar Oyo” inji Dansanda.

Sai dai wani lauya mai zaman kansa, Adewale Mosadomi ya bayyana a gaban kotu da nufin kare wanda ake kara, amma kotun bata gamsu ba, inda Alkalin kotun, E. Idowu ya bayyana cewa kotun bata da hurumin sauraron karar.

Don haka Alkali Idowu ya mika shari’ar zuwa ofishin babban jami’I mai shigar da kara na jahar Oyo domin samun shawarar kwararru, daga karshe kuma y adage sauraron karar zuwa ranar 6 ga watan Maris na shekarar 2019.

A wani labarin kuma, hukumar nan ta gwamnatin tarayya dake yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC ta fara tattara bayanai domin soma bincikar kudaden da aka fidda domin gyaran wutar lantarki lokacin gwamnatin Obasanjo.

Kamar dai yadda muka samu, kudaden da gwamnatin ta fitar a wancen lokacin domin aiwatar da wasu kwangilolin gina tashoshin samar da wutar lantarkin sun kai kimanin dala bilyan 16 daga 1999 zuwa 2007, wato lokacin mulkin Obasanjo.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Online view pixel