Muhimman abubuwa 7 a kan sabon Alkalin Alkalai, Ibrahim Tanko

Muhimman abubuwa 7 a kan sabon Alkalin Alkalai, Ibrahim Tanko

Shugaba Muhammadu Buhari ya nada Justice Ibrahim Tanko Muhammad a matsayin mukadashin Alkalin Alkalai na Najeriya.

Wannan ya biyo bayan dakatar da tsohon Alkalin Alkalai Walter Onnoghen ne da shugaban kasar ya yi a ranar Juma'a bisa umurnin kotun da'ar ma'aikata CCT.

Legit.ng ta kawo muku wasu muhimman abubuwa da ya dace ku sani a kan Justice Muhammad kamar yadda muka samu daga shafinsa na tattara bayanai na Wikipedia.

Muhimman abubuwa 7 da ya dace ka sani a kan sabon Alkalin Alkalai, Ibrahim Tanko
Muhimman abubuwa 7 da ya dace ka sani a kan sabon Alkalin Alkalai, Ibrahim Tanko
Asali: Facebook

1. An haifi Justice Muhammad ne a ranar 31 ga watan Disambar 1953 a karamar hukumar Doguwa-Giade da ke jihar Bauchi

2. Ya yi karatu a makarantar sakandare na Azare inda ya samu takardan WAEC a 1973 kafin ya wuce zuwa jami'an Ahmadu da ke Zaria inda ya kammala karatun digiri a fanin Shari'a a 1980.

3. Daga bisani ya yi digiri na biyu (Msc) da digiri na uku (PhD) duk a jami'an Ahmadu Bello da ke Zaria a 1984 da 1998.

4. An nada shi a matsayin lauya a 1981 sannan ya fara aiki a shekarar 1981.

DUBA WANNAN: Jigo a jam'iyyar APC ya fadi su waye ke tsoron tazarcen Buhari

Wannan ya biyo bayan dakatar da tsohon Alkalin Alkalai Walter Onnoghen ne da shugaban kasar ya yi a ranar Juma'a bisa umurnin kotun da'ar ma'aikata CCT.

Legit.ng ta kawo muku wasu muhimman abubuwa da ya dace ku sani a kan Justice Muhammad kamar yadda muka samu daga shafinsa na tattara bayanai na Wikipedia.

1. An haifi Justice Muhammad ne a ranar 31 ga watan Disambar 1953 a karamar

5. A 1989, an nada shi babban kotun majistare na babban birnin tarayya Abuja inda ya yi aiki har zuwa lokacin da aka nada shi Alkali a Kotun Shari'a na daukaka kara da ke Bauchi.

6. Ya cigaba da aiki a matsayin Alkali a Bauchi na tsawon shekaru 13 sannan aka nada shi Alkali a Kotun Koli ta kasa a 2006 amma ya fara aiki a ranar 7 ga Janairun 2007.

7. A ranar 25 ga watan Janairun 2019, Shugaba Muhammadu Buhari ya nada shi mukadashin Alkalin Alkalai bayan dakatar da Justice Walter Onnoghen.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164