Muhimman abubuwa 7 a kan sabon Alkalin Alkalai, Ibrahim Tanko
Shugaba Muhammadu Buhari ya nada Justice Ibrahim Tanko Muhammad a matsayin mukadashin Alkalin Alkalai na Najeriya.
Wannan ya biyo bayan dakatar da tsohon Alkalin Alkalai Walter Onnoghen ne da shugaban kasar ya yi a ranar Juma'a bisa umurnin kotun da'ar ma'aikata CCT.
Legit.ng ta kawo muku wasu muhimman abubuwa da ya dace ku sani a kan Justice Muhammad kamar yadda muka samu daga shafinsa na tattara bayanai na Wikipedia.
1. An haifi Justice Muhammad ne a ranar 31 ga watan Disambar 1953 a karamar hukumar Doguwa-Giade da ke jihar Bauchi
2. Ya yi karatu a makarantar sakandare na Azare inda ya samu takardan WAEC a 1973 kafin ya wuce zuwa jami'an Ahmadu da ke Zaria inda ya kammala karatun digiri a fanin Shari'a a 1980.
3. Daga bisani ya yi digiri na biyu (Msc) da digiri na uku (PhD) duk a jami'an Ahmadu Bello da ke Zaria a 1984 da 1998.
4. An nada shi a matsayin lauya a 1981 sannan ya fara aiki a shekarar 1981.
DUBA WANNAN: Jigo a jam'iyyar APC ya fadi su waye ke tsoron tazarcen Buhari
Wannan ya biyo bayan dakatar da tsohon Alkalin Alkalai Walter Onnoghen ne da shugaban kasar ya yi a ranar Juma'a bisa umurnin kotun da'ar ma'aikata CCT.
Legit.ng ta kawo muku wasu muhimman abubuwa da ya dace ku sani a kan Justice Muhammad kamar yadda muka samu daga shafinsa na tattara bayanai na Wikipedia.
1. An haifi Justice Muhammad ne a ranar 31 ga watan Disambar 1953 a karamar
5. A 1989, an nada shi babban kotun majistare na babban birnin tarayya Abuja inda ya yi aiki har zuwa lokacin da aka nada shi Alkali a Kotun Shari'a na daukaka kara da ke Bauchi.
6. Ya cigaba da aiki a matsayin Alkali a Bauchi na tsawon shekaru 13 sannan aka nada shi Alkali a Kotun Koli ta kasa a 2006 amma ya fara aiki a ranar 7 ga Janairun 2007.
7. A ranar 25 ga watan Janairun 2019, Shugaba Muhammadu Buhari ya nada shi mukadashin Alkalin Alkalai bayan dakatar da Justice Walter Onnoghen.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng