Mahaifiyar fitaccen dan kwallon kafa na Najeriya, Ahmed Musa, ta riga mu gidan gaskiya

Mahaifiyar fitaccen dan kwallon kafa na Najeriya, Ahmed Musa, ta riga mu gidan gaskiya

- Sarah Moses, mahaifiyar fitaccen dan kwallon kafa, Ahmed Musa, ta riga mu gidan gaskiya

- Mahaifiyar Ahmed Musa ta riga mu gidan gaskiya bayan ta sha fama da wata 'yar takaitacciyar rashin lafiya

- Ahmed Musa ya ce yau ita ce rana mafi munin bakin ciki a rayuwar sa

A yanzu din nan mun samu rahoton cewa, Sarah Moses, mahaifiyar fittacen dan wasan kwallon kafa na Najeriya, Ahmed Musa, ta riga mu gidan gaskiya a garin Abuja bayan ta sha fama da wata 'yar gajeruwar rashin lafiya.

Ahmed Musa wanda a halin yanzu ya ke taka leda a wata kungiyar kwallon kafa ta kasar Saudiyya, shine ya bayar da sanarwar wannan rahoto na bakin ciki a shafin sa na zauren sada zumunta.

Mahaifiyar fitaccen dan kwallon kafa na Najeriya, Ahmed Musa, ta riga mu gidan gaskiya
Mahaifiyar fitaccen dan kwallon kafa na Najeriya, Ahmed Musa, ta riga mu gidan gaskiya
Asali: Instagram

Kamar yadda rahotanni suka bayyana, Marigayi Sarah ta riga mun gidan gaskiya a yau Alhamis 24 ga watan Janairu bayan da sha fama da jinya wani asibiti da ke babban birnin kasar nan na tarayya.

Gabanin cikawar ta, fitaccen ya wallafa wasu sakonni a shafukan sa na zauren sada zumunta, inda ya ke bayyana damuwar sa gami da fatan waraka ga mahaifiyar sa da take fama da rashin lafiya.

KARANTA KUMA: Cikin Hotuna: An tafka mummunan hatsarin Mota a jihar Legas

Dan wasan ya ce a yau wannan rana ita ce mafi muni a rayuwar sakamakon bakin cikin da ya ke ciki a halin na rashin mahaifiya. Ya ce kewar ta da zai yi ta wuce misali.

Cikin wani rahoton da jaridar Legit.ng ta ruwaito, a wannan mako ne fitaccen dan wasan na kungiyar kwallon kafa ta Juventus wato Cristiano Ronaldo, ya amsa laifin sa na zargin kauracewa biyan haraji yayin da ya shura tamola a kasar Spain.

Sanarwa: Ku ci gaba da kasancewa tare da mu yayin da Shafin Naij.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Domin shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Ku biyo cikin shafukan mu na zaurukan sada zumunta:

https://facebook.com/legitnghausa

https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel