Siyasar 2019: Fitattun jaruman Kannywood 20 da zasu yiwa Buhari yakin neman zabe
A yayin da babban zaben shekarar 2019 ke kara katowa, yan siyasa daban daban da masu neman darewa madafan iko sun fara hada alaka da sashe na al’umma daban daban don cimma wannan buri nasu, tun daga matasa, dattawa, kungiyoyin mata, yan kasuwa da sauransu.
Sai dai da yake harkar fina finan Hausa na da matukar tasiri a yankin Arewacin Najeriya, hakan tasa masu shiryawa ko fitowa a cikin fina finan suka yi suna, tare da shahara ta hanyar daukakar da Allah yayi musu a wannan harka.
KU KARANTA: Kalli wasu mutane 4 da Ganduje zai nada mukaman Kwamishinoni a gwamnatinsa
A sanadiyyar wannan daukaka da suka samu ne yasa yan siyasa ke gogoriyon janyosu a jiki domin shafan hasken taurarinsu, ta yadda zasu dinga gayyatarsu zuwa tarukan yakin neman zabensu, da kuma nema su buga musu wakoki da zasu kambamasu.
Shima a nan shugaban kasa Muhammadu Buhari ba’a barshi a baya ba, inda uwargidarsa, Hajiya Aisha Buhari ta gayyato masa wasu fitattun jaruman Kannywood da zasu tallata shi tare da taya shi yakin neman zabe don cika burinsa na tazarce a zaben watan Feburairu.
Daga cikin wadannan shahararrun fuskokin da aka saba ganinsu a talabijin akwai;
Ali Nuhu
Adam A. Zango
Aminu Ala
Fati Abdullahi Washa
Halima Atete
Rukayya Dawaiyya
Maryam Yahaya
Ali Isa Jita
Husainin Danko
Adamu Nagudu
Abubakar Sani
Jamila Nagudu
Fati Shi’uma
Hauwa Waraka
Shehu Hassan Kano
Ladidi Fagge
Suleiman Bosho
Dan Auta
Rabiu Rikadawa
Hajara Usman
Sauran sun hada da Aminu Saira, Baban Chinedu, Yahaya Makaho, Sadi Sadi, Ado Gwanja, Fati Niger, Sadiq Mafia, Zuwaira Isma’il, Murja Baba, Hankaka, Sani Garba S.K, Ladidi Tubales, Haj Maryam CTV, Ibrahim Maishinku, Alhasan Kwalle, Rashida Adamu maisa’a, Bello Mohammed Bello, Sadiq Sani Sadiq, Naziru Ahmad da Falalu A Dorayi
Baya ga wadannan jarumai, akwai saura da dama, wadanda adadinsu ya haura mutane hamsin wadanda Aisha Buhari ta daukesu haya don ganin sun tallata hajar da maigidanta shugaba Buhari ya kasa a gabanin zaben 2019.
Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa
ko a http://twitter.com/legitcomhausa
KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki
Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com
Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa
Asali: Legit.ng