2019: Tawagar yakin neman zaben Atiku ta dira Sokoto

2019: Tawagar yakin neman zaben Atiku ta dira Sokoto

Kamar yadda ta sanar a jadawalin tsare-tsarenta na yakin neman zaben shugaban kasa, ayarin kamfen din dan takarar shugaban kasa a karkashin jam'iyyar PDP ya dira a jihar Sokoto, arewa maso yammacin Najeriya, domin kaddamar da kamfe din zaben Atiku.

Jam'iyyar ta PDP za ta fara kaddamar da yakin neman zabe ne a jihar Sokoto, kamar yadda darektan yada labarai na kamfen din Atiku kuma kakakin jam'iyyar PDP, Kola Ologbondiyan, ya sanar.

A sanarwar da kwamitin kamfen din Atiku ya fitar a jiya, Asabar, ya ce kwamitin yakin neman zaben zai tattauna da ma su zabe da niyyar nusar da su kalubalen da Najeriya ke fuskanta da kuma yadda Atiku ke shirin magance su.

2019: Tawagar yakin neman zaben Atiku ta dira Sokoto
Tawagar yakin neman zaben Atiku a Sokoto
Asali: Facebook

A cikin sanarwar da ta fitar, PDP ta ce babu yankin da ya fuskanci koma baya a karkashin gwamnatin APC kamar yankin arewa maso yamma da shugaba Buhari ya fito tare da bashi kuri'u ma fi yawa a zaben shekarar 2015.

DUBA WANNAN: Tsakanin Atiku da gwamnonin PDP: Har yanzu da sauran rina a kaba

"A cikin shekaru uku, babu wani cigaba da za a nuna shi da sunan cewar Buhari ya kawowa yankin arewa maso yamma. Duk gudunmawar da yankin ya bayar ta tashi a banza domin shugaba Buhari bai kara waiwayen yankin ba tun bayan hawansa mulki a shekarar 2015," a cewar jam'iyyar PDP.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng