An kori mutum 50 daga ofishin jakadancin Najeriya a Ingila, ko me yayi zafi?
- An kori ma'aikata sama da 50 a ofishin jakadancin kasar nan a kasar Ingila
- An nemi dasu karbi takaddar barin su aiki a ranar 23 ga watan Nuwamba
- An koresu ne saboda sun nemi a biyasu albashin su

Asali: Facebook
Wani rahoto ya bayyana cewa an kori ma'aikatan Najeriya sama da 50 a birnin London, masu aikin jakadanci maqale da Ministare ta huldar kasashen waje dake Abuja.
Rayuwa dai na da tsanani idan mutum ya rasa aikinsa, kuma akwai alamar asiri zai tonu tunda ba a kasar su suke ba.
Bayan sallamar tasu an nemi dasu karbi takaddar barin su aiki a ranar 23 ga watan Nuwamba.
Kafin yanzu dai ma'aikatan sun bayyana cewa ba'a biyasu albashin wannan shekara 2018 ba gaba daya, inda takaddar kokar ke nuni da cewa an sallame sune a dalilin rigima da sukeyi akan ayi maza a biya su albashin su.
DUBA WANNAN: Atiku ya wahal damu saboda cuwa-cuwarsa - Oby Ezeks
Daya daga cikin ma'aikatan da aka kora yace" suna bukatar duniya taga yanda akayi musu rashin adalci aka koresu dan kawai sun nemi a biyasu hakkinsu".
Sannan sunyi kira ga shugaban kasa Muhammad Buhari da yayi duba akan lamarin su.
Sanarwa: Shafin Naij.com Hausa shine yanzu ya koma Legit.ng Hausa, don inganta muku zafafan labarai dama kayatarwa
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/hausa.legit.ng
Twitter: https://twitter.com/hausa.legit.ng
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng