Mata za su samu tallafin akuyoyi da bunsuru 47,544 daga gwamnatin jihar Jigawa

Mata za su samu tallafin akuyoyi da bunsuru 47,544 daga gwamnatin jihar Jigawa

Gwamna Muhammadu Badaru na jihar Jigawa ya ce gwamnatinsa za ta rabawa mata 15,848 akuyoyi 47,544 a watan Yunin 2019 a karkashin shirin kiwon akuyoyi na Bankin bayar da bashi ga masu karamin karfi na jihar.

Badaru wanda ya yi magana da manema labarai a ranar Litinin a Dutse ya ce wannan tallafin yana cikin shirin jihar na tallafawa al'umma ta fanin kiwon dabobi.

A cewarsa, mata 8,428 sun karbi akuyoyi 25,284 a karkashin shirin a shekarar 2018.

Gwamnatin Jigawa za ta bawa mata tallafin akuyoyi da bunsuru 47,544
Gwamnatin Jigawa za ta bawa mata tallafin akuyoyi da bunsuru 47,544
Asali: Depositphotos

DUBA WANNAN: An sako Buhari a gaba a kan satar basira a salon kamfen dinsa

Ya ce shirin bayar da tallafin dabobin shine shirin bayar da bashi da mafi nasara a jihar inda ya ce 92% suna cigaba da kiwon kuma 79% sun biya bashin da aka basu.

A fanin noma kuma, gwamnan ya ce sauye-sauyen da gwamnatinsa ta kawo ya janyo hankalin masu saka hannun jari zuwa jihar daga gida Najeriya da ma kasashen waje.

"A halin yanzu, Dangote yana gina kamfanin sarrafa shinkafa a Kaugama da za ta rika samar da ton 280 na shinkafa a kowanne shekar idan an kammala.

"Kazalika, kamfanin Lee na saka hannun jari wajen noman rake a fili mai girman hecta 12,000 domin samar da raken da kamfanin ta zai rika samar da suga ton 120,000 a duk shekara.

"Kamfanin kuma zai rika samar wasu abubuwa masu amfani kamar taki ga manoma, wutar lantarki, mazarkwaila da dankulen maggi," inji Badaru.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel