Masu karbar fansho naso suma a tuna dasu a basu nasu hakkin
- Bayan an gama rigimar albashi, a tuna damu
- Masu karbar Fansho na kokawa kan kin biyansu hakkokinsu
- Ko karin albashin zai shaf su?

Asali: Depositphotos
A zantawa da suka yi da sashen Hausa na BBC, 'yan fansho sun roki gwamnatoci na jiha da Tarayya, da ma na kananan hukumomi, da suyi wa Allah su tuna dasu lokacin da ake biyan albashi wanda aka qara wa ma'aikata.
A cewarsu, sun gaji da jiran a biya su hakkokinsu na aiki tun bayan wancan karin, ballantana ma wai ace an kara albashin.
Ya zuwa yanzu dai, babu wanda yasan nawa za'a tashi dashi bayan da gwamnati ta zame tace shugaba Buhari bai gama sahalewa N30,000 din da ake biki a kai ba.
DUBA WANNAN: Yadda aka yi da Oshiomhole a oishin DSS
Su kuma 'yan fansho, basu gama sanin ko nawa zasu tashi dashi ba a qarin, kuma akwai basussuka musamman a jihohi da aka kasa biyansu tun wancan karin a 2010, lokacin duniya na kwance.
Sanarwa: Shafin Naij.com Hausa shine yanzu ya koma Legit.ng Hausa, don inganta muku zafafan labarai dama kayatarwa
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/hausa.legit.ng
Twitter: https://twitter.com/hausa.legit.ng
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng