Za'a biya diyyar Khashoggi daga lalitar gwamnati a Saudiyya

Za'a biya diyyar Khashoggi daga lalitar gwamnati a Saudiyya

- Kasar Saudia zata biya diyyar dan jarida daya mutu

- Ance za'a kuma maidowa iyalanshi gawarshi

- An nemi shi an rasa kafin daga bisani a gano kashe shi aka yi

Za'a biya diyyar Khashoggi daga lalitar gwamnati a Saudiyya
Za'a biya diyyar Khashoggi daga lalitar gwamnati a Saudiyya
Asali: Depositphotos

Kasar Saudia ta bayyana cewa zata biya diyyar dan jarida daya rasa ransa a lokacin da yake ziyartar ofishin jakadancin kasarsa a Turkiyya.

A yayin wata tattaunawa da CNN tayi da iyalan mamacin Salah da Abdallah sunce a dawo musu da gawar mahaifin su domin a binneshi a kasar sa wato Medina dake kasar Saudi Arabia, sannan sunce sun yadda da sarki Salman akan kokarin binciko wadanda sukayi wannan aika aika don a hukuntasu.

Wannan nuna rashin tausayi na kashe Kashoggi ya taba shugaban cin sarkin na Saudia.

DUBA WANNAN: 'Yan shia na kokarin zare ma soji ido da lasar takobi

Haspel wanda ya ziyarci kasar ta Turkey a watan daya gabata dangane da bincike akan mutuwar Kashoggi yace an bada umarnin kashe shi ne daga wasu manya na kasar Saudi.

A ranar Litinin ne gwamnatin Turkey ta bayyana cewa an tura wasu mutane 11 a 11 ga watan October wanda yayi dadai da kwanaki 9 da bacewar Kashoggi bayan ya shiga ofishin jakadancin Saudia don amsar takaddar izinin auren Cengiz wadda ta kasance yar kasar Turkey.

Sanarwa: Shafin Naij.com Hausa shine yanzu ya koma Legit.ng Hausa, don inganta muku zafafan labarai dama kayatarwa

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/hausa.legit.ng

Twitter: https://twitter.com/hausa.legit.ng

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng