Hotunan makaman da aka kama 'yan Shi'a da su a Abuja

Hotunan makaman da aka kama 'yan Shi'a da su a Abuja

- A jiya, Talata, ne aka yi wani kazamin artabu tsakanin jami'an rundunar 'yan sandan Najeriya da mabiya Shi'a a Abuja

- Hukumar ta 'yan sanda ta yi bajakolin mabiya Shi'ar da ta kama tare da makaman da ta samu a tare da su

- 'Yan Shi'ar sun kona daya daga cikin motocin jami'an 'yan sanda yayin rikicin na jiya

A jiya, Talata, ne aka yi wani kazamin artabu tsakanin jami'an rundunar 'yan sandan Najeriya da mabiya Shi'a a Abuja.

A yayin gwabzawar, jami'an 'yan sanda sun yi nasarar cafke mabiya Shi'a kimanin 400 tare da tsare su a ofishinsu.

Hukumar ta 'yan sanda ta yi bajakolin mabiya Shi'ar da ta kama tare da makaman da ta samu a tare da su.

Daga cikin irin wadannan makamai da aka samu a wurin mabiya Shi'ar akwai bam din kalanzir na kwalba da miyagun kwayoyi da ke birkice tunani.

Hotunan makaman da aka kama 'yan Shi'a da su a Abuja
Hotunan makaman da aka kama 'yan Shi'a da su a Abuja
Asali: Facebook

Hotunan makaman da aka kama 'yan Shi'a da su a Abuja
Hotunan makaman da aka kama 'yan Shi'a da su a Abuja
Asali: Facebook

Hotunan makaman da aka kama 'yan Shi'a da su a Abuja
Motar 'yan sanda da 'yan Shi'a da su ka kone a Abuja
Asali: Twitter

'Yan Shi'ar sun kona daya daga cikin motocin jami'an 'yan sanda yayin rikicin.

Ko a ranar Litinin sai da dakarun sojin Najeriya su ka budewa wasu 'yan Shi'a wuta bayan sun tare hanyar da motar sojoji dauke da malamai za ta wuce a kan titin Nyanya.

DUBA WANNAN: Alkawarin da Buhari ya yiwa 'yan takarar APC da su ka fadi a zaben cikin gida

Haka a ranar Juma'a ta makon jiya aka kara samun kwatankwacin irin wannan rikicin tsakanin dakarun soji da mabiya Shi'ar a daidai Zuba, kan hanyar shiga Abuja.

Duk da wannan gwabzawa, mabiya Shi'ar sun ce ba zasu daina zanga-zanga ba har sai an sako jagoransu, Sheikh Ibrahim El-Zakzaky, da gwamnati ke tsare da shi tun shekarar 2015.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng