Jonathan ya gayyaci Buhari, Atiku da Obasanjo taron kaddamar da littafin sa
- Tsohon Shugaban kasa Jonathan zai buga wani sabon littafin sa kwanan nan
- Sunan wannan littafi da za a buga a karshen watan gobe ‘My Transition Hours’
- Tsohon Shugaban ya gayyaci Muhammadu Buhari da su Obasanjo wajen taron

Asali: Facebook
Labari ya zo mana cewa tsohon Shugaban kasa Dr. Goodluck Jonathan zai buga wani littafi game da lokacin mulkin sa kwanan nan. Jonathan ya gayyaci irin su tsohon Shugaba Olusegun Obasanjo zuwa wajen kaddamar da littafin.
Haka zalika Goodluck Jonathan ya gayyaci Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da kuma Abokin takarar sa da za su gwabza a 2019 watau Atiku Abubakar wajen wannan taro da za a fito da littafin sa mai suna ‘My Transition Hours’
KU KARANTA: Saboda yadda Jonathan ya sallama mulki ya sa na ke kallon sa da mutunci – Buhari
Jonathan zai kaddamar da wannan littafi ne a Ranar 20 ga Watan Nuwamba wanda ya zo daidai da ranar da zai cika shekaru 61 a Duniya. Littafin zai kunshi labarin yadda ya sha kasa a zaben 2015 da kuma yadda ya mika mulki.
Tsohon Shugaban ya gayyaci manyan Kasar nan irin su tsohon Alkalin Alkalai Salihu Alfa Belgore, da Janar Theophilus Y. Danjuma wajen kaddamar da wannan littafi. Mai Girma Gwamna Seriake Dickson shi ne mai masaukin baki.
Har wa yau, Jonathan ya gayyaci tsofaffin Shugaban Kasashen Afrika Alassane Ouattara na Ivory Coast da kuma Shugaba John Dramani Mahama wanda ya rubuta masa mukaddima wajen bikin kaddamar da wani babban littafi a Abuja.
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.naij.com
Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa
Ko a http://twitter.com/legitnghausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Asali: Legit.ng