Hotuna: Daga dawowa, Zanga-zanga ya barke majalisar dokokin tarayya
Hadiman yan majalisun wakilai da dattawan Najeriya kuma ma’aikatan majalisar sun kaddamar da zanga-zangan lumana kan bashin alawus da suke bi na tsawon shekaru uku yanzu.
Ma’aikatan sun gudanar da zanga-zangan ne a harabar majalisar dokokin inda suka wakokin zanga-zanga rike da takardu masu rubutu akansu mai cewa, “Mu hadimai ne, ba bayi ba”.
Majalisar dattawa ta dawo bakin aiki yau kuma ba tare da dadewa ba suka koma ganawar cikin gida inda shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki, ya jagoranta.
Nyakari-Abasi Etuk, wanda ya jagoranci zanga-zangar ya bayyanawa manema labarai cewa ba’a biyasu alawus ba tun lokacin da Saraki ya zama shugaban majalisar.
Sanarwa: Shafin Legit.ng Hausa zai koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa damu.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa
Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng