El-Rufai ya karrama wani attajri da ya dauki nauyin daiban jahar Kaduna

El-Rufai ya karrama wani attajri da ya dauki nauyin daiban jahar Kaduna

Gwamnan jahar Kaduna Malam Nasir Ahmad El-Rufai ya karrama wani shahararren attajiri mai karfin arziki, kuma surukin shugaban kasa Muhammadu Buhari, Alhaji Muhammad Indimi, inda ya shirya masa waliman karramawa a Kaduna.

Legit.ng ta ruwaito El-Rufai ya shirya ma Indimi wannan walima ne a fadar gwamnatin jahar dake gidan Sir Kashim Ibrahim a ranar Alhamis din data gabata 4 ga watan Oktoba don bayyana godiyar gwamnatin jahar game da kokarinsa na taimakawa gajiyayyu.

KU KARANTA: Takarar shugaban kasa: Gwamna Tambuwal ya yi mubaya’a ga Atiku Abubakar

El-Rufai ya karrama wani attajri da ya dauki nauyin daiban jahar Kaduna
El-Rufai
Asali: Facebook

Haka zalika a jawabinsa, Gwamna El-Rufai ya bayyana farin cikinsa da godiyar al’ummar jahar Kaduna gaba daya game da daukan nauyin karatun daliban jahar Kaduna su ashirin a fannoni daban daban a jami’ar International University of Africa dake kasar Sudan.

A kokarinsa na jin jina ma Attajirin, gwamnan jahar Kaduna ya mika masa wata lambar yabo domin gode masa bisa gudunmuwar da yake baiwa jahar Kaduna, musamman a fannin ilimi

El-Rufai ya karrama wani attajri da ya dauki nauyin daiban jahar Kaduna
El-Rufai
Asali: UGC

Shima a nasa jawabin, Alhaji Muhammed Indimi ya gode ma gwamnatin jahar Kaduna a karkashin jagorancin Gwamna Nasir El-Rufai bisa karramawar da aka yi masa, sa’annan yayi alkawarin kara daukan nauyin karatun dalibai mata daga Kaduna a fannin likitanci.

Muhammed Indimi yace zai dauki nauyin dalibai matan ne domin bada gudunmuwarsa ga cigaban ilimin kata ta hanyar basu damar samun guraben karatu daban daban.

El-Rufai ya karrama wani attajri da ya dauki nauyin daiban jahar Kaduna
El-Rufai
Asali: Facebook

Idan za’a tuna a shekarar data gabata ne yaron Muhammed Indimi, Ahmed Indimi ya auri diyar shugaban kasa Muhammadu Buhari, Zara Buhari, wanda a yanzu haka rahotanni suka tabbatar da cewa tana dauke da juna biyu.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

ko a http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.ng Hausa cikin sauki https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Sanarwa: Shafin Legit.ng Hausa za ta koma LEGIT.ng Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng