Soyayya gamon jini: Wani dan shekara 19 ya auri 'yan shekara 39 a Najeriya

Soyayya gamon jini: Wani dan shekara 19 ya auri 'yan shekara 39 a Najeriya

Soyayya, Hausawa suka ce gamon jini ce kuma wata aba ce mai matukar muhimmaci a rayuwar 'yan adam dake a doron duniya. Haka zalika dai Hausawa na cewa ribar soyayya daman can aure ce.

Idan ana maganar soyayya to fa daman dole ne akan samu labarai na ban al'ajabi a wani lokacin kuma ma hadda mamaki musamman duba da cewa akan samu wasu lokuta da ta kan zo da abubuwan mamaki.

Soyayya gamon jini: Wani dan shekara 19 ya auri 'yan shekara 39 a Najeriya
Soyayya gamon jini: Wani dan shekara 19 ya auri 'yan shekara 39 a Najeriya
Asali: Facebook

KU KARANTA: An umurci jami'an tsaro su kawo karshen rikicin Filato

A bisa al'ada dai miji ko saurayi kan fi mata ko budurwa girma ko da kuma da shekaru ne kadan duk kuwa da cewa akan yi tsogwami idan har shekarun miji suka zarce na mata sosai.

To kwatsam kuma sai ga wani labarin soyayyar da ya dauki hankalin al'umma da dama na wani matashi mai shekaru 19 kacal a duniya da ya auri wata mata mai shekaru 39 watau dai wadda ta girme shi da shekaru 20. Tirkashi!

Labarin wannan abun mamakin dai ya fallasa ne bayan da wani bawan Allah ya shelanta hakan a shafin sa na dandalin sadarwar zamani na Facebook tare ma da yada hotunan ma'auratan.

Ga dai hotunan nan:

Soyayya gamon jini: Wani dan shekara 19 ya auri 'yan shekara 39 a Najeriya
Soyayya gamon jini: Wani dan shekara 19 ya auri 'yan shekara 39 a Najeriya
Asali: Facebook

Soyayya gamon jini: Wani dan shekara 19 ya auri 'yan shekara 39 a Najeriya
Soyayya gamon jini: Wani dan shekara 19 ya auri 'yan shekara 39 a Najeriya
Asali: Facebook

Soyayya gamon jini: Wani dan shekara 19 ya auri 'yan shekara 39 a Najeriya
Soyayya gamon jini: Wani dan shekara 19 ya auri 'yan shekara 39 a Najeriya
Asali: Facebook

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng