Gwamna Shettima ya lashe tikitin takarar sanata a APC

Gwamna Shettima ya lashe tikitin takarar sanata a APC

Gwamnan jihar Borno, Alhaji Kashim Shettima, ya mallaki tikitin takarar kujerar sanata na yankin Borno ta tsakiya karkashin jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

Yayi nasara a zaben fidda gwani wanda aka gabatar a ranar Laraba, 3 ga watan Oktoba wanda aka sanar da sakamakon a safiyar yau Alhamis, 4 ga watan Oktoba.

Ya samu kuri’u 2,735 inda ya doge abokin takararsa Alhaji Ali Wurge wanda ya samu kuri’u biyar.

Gwamna Shettima ya lashe tikitin takarar sanata a APC
Gwamna Shettima ya lashe tikitin takarar sanata a APC
Asali: Depositphotos

Yayida yake jawabi jim kadan bayan an kaddamar das hi a matsayin mai nasara, yayi godiya ga magoya bayansa akan imani da suka yi da shi.

Sanata Babakaka Garbai wanda a yanzu shine sanata mai wakiltan Borno ta tsakiya a majalisar dokokin kasar ne ya tsaya a matsayin wakilin Shettima a zaben.

A baya Legit.ng ta rahoto cewa an zabi Gwamna Umaru Al-Makura a matsayin dan takarar kujeran sanata na Nasarawa ta kudu a zaben 2019 karkashin jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

KU KARANTA KUMA: Sabon rikici ya kunno kai a APC: An ruro ma Oshiomhole wuta cewa yayi murabus daga matsayinsa

Shugaban kwamitin zaben, Ismaila Ahmed, wanda ya samu wakilcin sakataren, Abdullahi Candido ya sanar da sakamakon zaben a ranar Laraba, 3 ga watan Oktoba, a Lafia, babban birnin jihar Nasarawa.

Ahmed yace Al-Makura ya samu kuri’u 1,262 inda ya kayar da abokin hamayyarsa, Sanata Salisu Egyegbola, wanda ya samu kuri’u 312.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin Legit.ng Hausa zai koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewar ku tare da mu.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng