Rikicin Ambode da APC a Legas: Buhari ya gana da Tinubu da Akande

Rikicin Ambode da APC a Legas: Buhari ya gana da Tinubu da Akande

A kokarin warware rikicin da ya dabaibaye takarar gwamna Ambode na jihar Legas a APC, shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya yi wata ganawar sirri da yammacin yau, Litinin, da jagoran jam’iyyar APC, Bola Tinubu, da kuma kuma shugaban riko na farko a jam’iyyar, Bisi Akande.

Duk da ganawar ta sirri ce, majiyar mu ta sanar da mu cewar ganawar na da nasaba da matsalar da gwamna Ambode ke fuskanta da Tinubu a kokarinsa na samun tikitin takara karkashin APC a karo na biyu.

Majiyar mu a fadar shugaban kasa ta kyara mana cewar shugaba Buhari na kokarin ganin an warware sabanin dake tsakanin Ambode da Tinubu domin samun hadin kan jam’iyyar APC a jihar Legas. Wata majiyar ta bayyana cewar Buhari na da ra’ayin a bar Ambode ya sake yin takara saboda irin kokarin day a yi ta fuskar shimfida aiyukan raya kasa a shekaru kusan hudu da ya yi a karagar mulki.

Rikicin Ambode da APC a Legas: Buhari ya gana da Tinubu da Akande
Ambode da Tinubu
Asali: Depositphotos

Sai dai babu tabbacin ko Tinubu ya yi na’am da wannan ra’ayi na shugaba Buhari, musamman ganin cewar tuni ya bayyana goyon bayansa ga Babajide Sanwa-Olu, abokin hamayyar Ambode.

DUBA WANNAN: Masu gudu sun dawo: Bala Kaura, tsohon ministan Abuja ya zama dan takarar gwamna a PDP

A ranar Asabar ne 'yan majalisar jihar Legas suka juya wa gwamna Akinwumi Ambode baya yayin da 36 cikin 40 na mambobin suka marawa Babajide Sanwo-Olu baya a matsayin dan takarar gwamnan jam'iyyar APC a zaben 2019.

'Yan majalisan sun bayyana matsayarsu ne bayan wata taro da su kayi a jiya, Asabar, karkashin jagorancin kakakin majalisar dokokin jihar Legas, Mudashiru Obasa, inda dukkan 'yan majalisar suka sanya hannu a takarda.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin Legit.ng Hausa zai koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng