Yanzu-yanzu: Mama Taraba ta yi murabus daga gwamnatin Buhari, ta fita daga APC (Karanta Wasikar)
Labarin da ke shigowa da dumi-dumi na nuna cewa ministar harkokin mata, Aisha Jummai Alhassan, wacce aka fi sani da Mama Taraba ta yi murabus daga kujerarta, sannan kuma ta fita daga jam'iyyar APC.
A ranan Alhamis, kwamitin gudanarwan jam’iyyar APC ta yanke shawaran hana Mama Taraba takaran kujeran gwamnan jihar Taraba karkashin jam’iyyarsu.
Wadanda abu ya janyo cece-kuce tsakanin al’umman jam’iyyar APC. Duk da cewa ba’a bayyana ainihin dalilin da yasa aka hanata tikitin jam’iyyar ba, alkaluma sun nuna cewa maganan da tayi na goyon bayan Atiku a 2019 ya janyo mata hakan.
Tace: “Na rubuta wannan wasikan ne domin sanar da shugaban kasa niyya ta na murabus daga kujeran minister Najeriya da kuma matsayin mambar jam’iyyar All Progressives Congress APC).”
Kalli hotunan wasikar:

Asali: Facebook

Asali: Twitter
KU KARANTA: Wasu Ministocin Buhari 7 da basu da takardar NYSC

Asali: Twitter
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng