Hotuna: Yadda zaben kato bayan kato ya gudana a jihar Kano
Manya da yara a jihar Kano sun fita kwansu da kwarkwartarsu domin zaben kato bayan kato na fitar da gwanin shugaban kasa karkashin jam'iyyar APC a yau Juma'a, 28 ga watan Satumba, 2018.
Gwamnan jihar, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya fito da makwabtansa manya da yara cikin layi domin kada kuri'arsa.
Hakazalika, mataimakin gwamnan jihar, Dakta Nasiru Yusuf Gawuna, ya fito da jama'arsa a Gawuna, karamar hukumar Nasarawa na jihar Kano.
Ba'a bar Kakakin majalisar dokokin jihar, Hanarabul Alhassan Rurum, a yabaya ba inda ya fito da jama'arsa domin kada kuri'arsu.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa
Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng