Hangen nasara: Magoya bayan PDP sun fara rera waka suna tikar rawar murna

Hangen nasara: Magoya bayan PDP sun fara rera waka suna tikar rawar murna

A jiya Asabar ne, 22 ga watan Satumba 2018, al'ummar jihar Osun suka gudanar da zaben gwamna da zai shugabancin jihar a shekaru 4 masu zuwa. Da misalin karfe 3:35 na safiyar yau, Lahadi ne hukumar INEC ta fara sanar da sakamakon zaben kowace karamar hukuma.

A kidaya na karshe, kafin shigowar sakamakon karamar hukumar Osogbo, Legit.ng ta kawo maku adadin kuri'un da kowacce jam'iyya ta samu kamar haka;

PDP

Yawan kuri'u: 254698

APC

Yawan kuri'u: 254345

SDP Yawan kuri'u:

128049

ADP

Yawan kuri'u: 49744

ADC

Yawan kuri'u: 7681

Ganin wannan sakamako ya saka masoya da magoya bayan jam'iyyar PDP da dan takarar ta fara murnar hangen samun nasara a zaben na jiya.

DUBA WANNAN: Alkiblar nasarar zaben gwamnan Osuna ta canja bayan shigowar sakamakon Osogbo

Duk da sakamakon karamar hukumar Osogbo da ake dako ya shigo hannu, ya zuwa yanzu hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ba ta fadi waye ya lashe zaben ba.

Hangen nasara: Magoya bayan PDP sun fara rera waka suna tikar rawar murna
Magoya bayan PDP a bakin cibiyar tattara sakamako
Asali: UGC

Hangen nasara: Magoya bayan PDP sun fara rera waka suna tikar rawar murna
Magoya bayan PDP sun fara rera waka suna tikar rawar murna
Asali: Original

Hangen nasara: Magoya bayan PDP sun fara rera waka suna tikar rawar murna
Magoya bayan PDP na rera waka suna tikar rawar murna
Asali: Original

Hangen nasara: Magoya bayan PDP sun fara rera waka suna tikar rawar murna
Magoya bayan PDP na rera waka suna tikar rawar murna
Asali: Original

Zaben gwamnan jihar ta Osun da ya gudana a jiya Asabar, na iya zama fitilar haska zaben 2019 kamar yadda jakan kungiyar kasashen turai da ke Nigeria ya bayyana, wanda kuma zai kawo karshen mulkin Ogbeni Rauf Aregbesola na tsawon shekaru 8.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel