El-Rufai, Lai sun isa jihar Osun gabannin zaben gwamna da za’a gudanar a gobe

El-Rufai, Lai sun isa jihar Osun gabannin zaben gwamna da za’a gudanar a gobe

Nasir El-Rufai, gwamnan jihar Kaduna, da ministan labarai, Lai Mohammed, a halin yanzu suna a Osogbo, babban birnin jihar Osun.

Sun sauka a jihar da misalin karfe 1:00pm sannan suka nufi gidan gwamnatin Okefia, Osogbo, inda suka samu tarba daga Rauf Aregbesola, gwamnan jihar.

Gwamnonin biyu tare da Mohammmed sun halarci sallar juma’a a masallacin gidan gwamnati.

El-Rufai, Lai sun isa jihar Osun gabannin zaben gwamna da za’a gudanar a gobe
El-Rufai, Lai sun isa jihar Osun gabannin zaben gwamna da za’a gudanar a gobe
Asali: Depositphotos

Akwai rahotanni dake nuni cewa Bola Tinubu, babban jigon APCna kasa ma yana a jihar.

Gboyega Oyetola, tsohon shugaban ma’aikata ga Aregbesola, ya kasance dan takaran jam’iyyar APC mai ci.

KU KARANTA KUMA: Sabani ya shiga tsakanin gwamnan Zamfara da mataimakinsa

Akwai yan takara 48 a zaben amman tseren na a tsakanin Oyetola, Ademola Adeleke na jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Iyiola Omisore na Social Democratic Party (SDP) da kuma Moshood Adeoti, na Action Democratic Party (ADP).

A baya Legit.ng ta rahoto cewa tsohon gwamnan Kano kuma dan takaran shugaban kasa a jam’iyyar Peoples Democratic Party, SanataRabiu Kwankwaso, yace yana da karfin bige shugaban kasa Muhammadu Buhari a zabe.

Ya kuma bayyana cewa zai tabbatar da ganin an samu zaman lafiya, matakan tsaro da kuma kayan more rayuwa idan har aka zabe shi a matsayin shugaban kasa a zaben kasa na 2019.

Ya fadi haka ne a ranar Juma’a, 21 ga watan Satumba a lokacin wani hira a Channels Television, inda yayi ikirarin cewa yana da mabiya da dama da zasu sa yayi nasara a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng