Da dumin sa: Jirgin kasa yayi hadari daga Abuja zuwa Kaduna, ya kashe wata mata

Da dumin sa: Jirgin kasa yayi hadari daga Abuja zuwa Kaduna, ya kashe wata mata

- Jirgin kasa yayi hadari daga Abuja zuwa Kaduna

- Ya kashe wata mata akan hanyar sa

- A kwanan baya ma jirgin ya kashe shanu 50

Jirgin kasan dake jigilar fasinjoji daga garin Abuja zuwa Kaduna a ranar Asabar yayi hadari kan hanyar sa daga garin Abuja zuwa Kaduna jim kadan bayan barin tashar sa dake a unguwar Idu, Kubuwa, birnin tarayya Abuja.

Da dumin sa: Jirgin kasa yayi hadari daga Abuja zuwa Kaduna, ya kashe wata mata
Da dumin sa: Jirgin kasa yayi hadari daga Abuja zuwa Kaduna, ya kashe wata mata
Asali: Depositphotos

KU KARANTA: An yi wa Buhari ca game da nade-naden sa

Majiyar mu dai ta tabbatar mana da cewa jirgin kasan dai haka zalika ya yi raga-raga da wata baiwar Allah inda ya markade ta ta yadda ba ma a gane ta kwata-kwata.

Legit.ng ta samu cewa a kwanan baya ma dai jirgin kasan yayi hatsari akan hanyar ta sa ta zuwa Abuja a cikin daji inda ya kashe akalla shanu sama hamsin na fulani suna tsakar kiwo.

A wani labarin kuma, Hafsan sojojin saman Najeriya Sadiq Abubakar ya bayyana cewa rundunar sa ta sayi akalla jiragen yaki talatin tun bayan hawan shugaba Muhammadu Buhari a karagar mulki kimanin shekaru uku da suka shude.

Hafsan sojin dai ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi a yayin bude wasu muhimman ayyuka a makarantar koyon aikin sojan saman ta Najeriya dake a garin Kaduna.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel