Sojojin Najeriya sun yi fata-fata da 'yan bindiga 10, mai satar mutane a Kaduna

Sojojin Najeriya sun yi fata-fata da 'yan bindiga 10, mai satar mutane a Kaduna

- Sojojin Najeriya sun yi fata-fata da 'yan bindiga 10, mai satar mutane a Kaduna

- Sun kashe su ne a kananan hukumomin Chikun da Birnin Gwari

Jami'an sojojin Najeriya na runduna ta daya dake a jihar Kaduna a ranar Alhamis ta sanar da samun nasarar yin fata-fata da akalla wasu da ake zargin 'yan bindiga ne su goma da kuma kama wani mai satar mutane daya a kananan hukumomin Chikun da Birnin Gwari, jihar Kaduna.

Sojojin Najeriya sun yi fata-fata da 'yan bindiga 10, mai satar mutane a Kaduna
Sojojin Najeriya sun yi fata-fata da 'yan bindiga 10, mai satar mutane a Kaduna
Asali: Facebook

KU KARANTA: 'Yan kasuwa sun kunyata Gwamna El-rufai

Mataimakin daraktan hulda da jama'a na rundunar ne dai mai suna Kanal Muhammad Dole shine ya sanar da hakan a cikin wata takardar manema labarai da ya rabawa a garin Kaduna.

Legit.ng ta samu cewa Kanal Muhammad Dole a cikin takardar sanarwar ta sa ya bayyana cewa akalla 'yan bindigar shida ne suka kashe a kauyukan Kidandan akan hanyar Dogon Dawa, Unguwar Bilya, Sofa da Unguwan Nakuli dukkan su a cu=ikin karamar hukumar Birnin Gwari daga 10 ga watan Satumba.

Haka zalika yace sauran wadanda jami'an sojojin suka yi fata-fata da su din sune a kauyukan Kidan Isa, Gidan Haruna Mobale da kuma Kuduru yayin da wasu kuma suka tsere da raunuka da dama a jikin su.

A wani labarin kuma, jami'an sojojin saman Najeriya dake a cikin rundunar hadin gwuiwa ta Lafiya Dole dake yaki da 'yan ta'addan Boko Haram a shiyyar Arewa maso gabashin kasar nan sun sanar da samun gagarumar nasara a kan 'yan ta'addan a maboyar su dake a dajin Sambisa.

Kamar yadda muka smu, rundunar ta bayyana cewa ta samu yin galaba akan 'yan ta'addan ne tare kuma da yin fata-fata da ma'ajiyar makaman a dajin na Sambisa dake zaman mafaka gare su.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng