Cikin hotuna: An kaddamar da taron FOCAC a birnin Beijing, kasar Sin
An kaddamar da taron hadin kansa nahiyar Afrika da kasar Sin karo na bakwai a babban farfajiyar taron na Great Hall of Fame da ke babban birnin kasar Sin, Beijing a yau Litinin, 3 ga watan Satumba, 2018.
Shugaba Muhammadu Buhari, shugaban kasar Sin, Xi Jingpin, da sauran shugabannin kasashen Afrika ne suke hallare a wannan babban taro.
Legit.ng ta kawo kuku rahoton cewa shugaba Muhammadu Buhari ya fara abubuwan da suka kaisa. Buhari ya gana da yan Najeriya mazauna kasar Sin da safiyar yau Lahadi, 2 ga watan Agusta, 2018 a ofishin jakadan Najeriy a kasar Sin.
A ganawarsa da su, Buhari ya bayyana musu cewa ko kadan ba ya tsoron gudanar da zaben gaskiya cikin zaman lafiya da lumana a 2019.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa
Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng