Wuta daga sama: Sojin saman Najeriya sun yi wa 'yan Boko Haram mummunar illa

Wuta daga sama: Sojin saman Najeriya sun yi wa 'yan Boko Haram mummunar illa

- Sojin saman Najeriya sun yi wa 'yan Boko Haram mummunar illa

- Hakan ta faru ne sakamako wani artabu da sukayi a garin Zari

- An kwace motoci da muggan makaman yan ta'addan

Jami'an rundunar sojin saman Najeriya dake a cikin rundunar hadakar fatattakar 'yan Boko Haram ta 'Lafiya Dole ta sanar da samun gagarumar nasara akan 'yan ta'addan a garin Zari dake a kan iyaka da tafkin Cadi, jihar Borno.

Wuta daga sama: Sojin saman Najeriya sun yi wa 'yan Boko Haram mummunar illa
Wuta daga sama: Sojin saman Najeriya sun yi wa 'yan Boko Haram mummunar illa
Asali: Depositphotos

KU KARANTA: Zaben 2019: Hafsan sojin Najeriya ya gargadi yan siyasa

Jami'ain hulda da jama'a na rundunar Air Commodore Ibikunle Daramola shine ya sanarwa da manema labarai hakan a ranar Juma'ar da ta gaba a garin Abuja babban birnin tarayya.

Legit.ng ta samu cewa kamar yadda ya shaidawa manema labaran, jami'an sojin saman sun samu nasarar ne a wani artabu da sukayi da 'yan Boko Haram din a ranar Alhamis din da ta gaba.

Air Commodore Ibikunle Daramola ya kuma kara da cewa sun kwace motoci da wasu mugganan makamai da dama daga hannun 'yan ta'addan.

A wani labarin kuma, Gwamnatin tarayyar Najeriya a karkashin jagorancin Shugaba Buhari ta ce ta kammala wani cikakken daftari dake dauke da tsare-tsaren yadda za'a habaka yankin Arewa maso gabas da 'yan ta'addan Boko Haram suka kassara.

Wakilin Najeriya na din-din-din a majalisar dinkin duniya Farfesa Tijjani Bande shine ya sanar da hakan a lokacin da yake tattaunawa da wasu mahalarta taron lalubo hanyoyin tabbatar da zaman lafiya da kuma farfado da tafkin Cadi na majalisar.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng