Shugaba Buhari ya isa 'Kasar Sin da safiyar yau ta Asabar

Shugaba Buhari ya isa 'Kasar Sin da safiyar yau ta Asabar

Mun samu cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya isa birnin Beijing na kasar Sin a safiyar yau ta Asabar domin halartar taron hadin kan kasar da kuma nahiyyar Afirka karo na bakwai da za a gudanar a ranakun 3 da 4 ga watan Satumba.

Hadimin shugaban kasar na sabuwar hanyar sadarwa, Bashir Ahmad, wanda ya kasance cikin tawagar shugaban kasar shine ya bayyana wannan sabon rahoto a shafin sa na dandalin sada zumunta.

Shugaba Buhari ya isa 'Kasar Sin da safiyar yau ta Asabar
Shugaba Buhari ya isa 'Kasar Sin da safiyar yau ta Asabar
Asali: Twitter

Shugaba Buhari ya isa 'Kasar Sin da safiyar yau ta Asabar
Shugaba Buhari ya isa 'Kasar Sin da safiyar yau ta Asabar
Asali: Twitter

Shugaba Buhari ya isa 'Kasar Sin da safiyar yau ta Asabar
Shugaba Buhari ya isa 'Kasar Sin da safiyar yau ta Asabar
Asali: Twitter

Shugaba Buhari ya isa 'Kasar Sin da safiyar yau ta Asabar
Shugaba Buhari ya isa 'Kasar Sin da safiyar yau ta Asabar
Asali: Twitter

Shugaba Buhari ya isa 'Kasar Sin da safiyar yau ta Asabar
Shugaba Buhari ya isa 'Kasar Sin da safiyar yau ta Asabar
Asali: Twitter

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya ya ruwaito cewa, shugaba Buhari yayi bankwana da birnin Abuja a ranar Juma'a da gabata inda ya nufaci Birnin Sin bayan ganawar sa da shugaban kasar Jamus, Angela Merkel a fadarsa ta Villa.

KARANTA KUMA: 'Yan Siyasa 8 da ake zargi da rashawar N232bn kuma suke fafutika akan tazarcen Buhari

Cikin wata sanarwa a ranar 30 ga watan Agustan da ta gabata, kakakin shugaban kasa, Mallam Garba ya bayyana cewa, shugaba Buhari zai gana da shugaban kasar na China, Xi Jin Ping, tare da sauran shugabannin Afirka kafin gudanar da babban taron.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Don shawara ko bamu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku duba shafukanmu na dandalin sada zumunta a:

https://business.facebook.com/pg/naijcomhausa

https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel