Babbar jam'iyyar adawa PDP ta bawa wani tsohon minista babban mukami

Babbar jam'iyyar adawa PDP ta bawa wani tsohon minista babban mukami

- Shugaban jam'iyyar PDP, Uche Secondus ya baiwa Cif Osita Chidoka, wani babban mukami a jam'iyyar

- Jam'iyyar ta bukaci Chidoka yayi amfani da ilimin shi da kwarewar shi wurin cigaban jam'iyyar

Babbar jam'iyyar adawa PDP ta bawa wani tsohon minista babban mukami
Babbar jam'iyyar adawa PDP ta bawa wani tsohon minista babban mukami
Asali: Depositphotos

Shugaban babbar jam'iyyar adawa ta Peoples Democratic Party (PDP), Uche Secondus ya baiwa tsohon ministan jiragen sama, sannan kuma tsohon shugaban hukumar kiyaye hadura na kasa, Cif Osita Chidoka, a matsayin mai bada shawara a fannin tsare - tsare.

DUBA WANNAN: An gudu ba a tsira ba: Wani Gwamna ya gudu daga APC, PDP kuma sun ce baza su ba shi tikitin takara ba

Sanarwar ta fito daga bakin Sakataren jam'iyyar a fannin watsa labarai na kasa, Kola Ologbondiyan ranar juma'ar nan a birnin Abuja.

"Chidoka, wanda ya kware a fannin tsare - tsare na ayyukan gwamnati, muna tunanin zai yi amfani da wannan kwarewar tashi, domin ciyar da jam'iyyar mu gaba," inji shi.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel