Takaitaccen tarihin Gwarzon ‘Dan wasan Najeriya Ahmed Musa

Takaitaccen tarihin Gwarzon ‘Dan wasan Najeriya Ahmed Musa

Gwarzon ‘Dan wasan nan na Kungiyar Super Eagles na Najeriya watau Ahmed Musa yayi suna a Duniya don haka mu ka kawo maku kadan daga cikin tarihin babban ‘Dan kwallon.

  • An haifi Ahmed Musa ne a Watan Oktoba a shekarar 1992 a Garin Jos da ke Jihar Filato. Tun yana ‘Dan shekara 14 dai Ahmed Musa ya fara nunawa Duniya irin kwarewar sa a Kulob din GBS da ke Jos.
Takaitaccen tarihin Gwarzon ‘Dan wasan Najeriya Ahmed Musa
Ahmed Musa ya taba rike kyaftin din Super Eagles
  • A shekarar 2007 ne aka fara sanin ‘Dan wasa Ahmed Musa a Duniya wanda hakan ta sa Kungiya kwallon kafa na JUTH da ke Jos ta dauke sa. A nan kuma Ahmed Musa ya kwallaye har 4 a shekarar.
  • Bayan JUTH ne Ahmed Musa ya koma Kungiyar Kano Pillars a matsayin ‘Dan wasan aro. A Kano Pillars ne dai Musa ya kafa tarihi ya ci kwallayen da ba a taba cin su ba a Gasar Firimiya na Najeriya.

KU KARANTA: Jakadan Ingila yayi magana game da Najeriya

  • A 2010 ne Musa ya koma Kungiyar Turai ta VVV Venlo sai dai bai iya fara bugawa ba sai da ya cika shekara 18 a Duniya. A wasan da ya fara bugawa kuwa ya nuna kan sa inda ya samowa Kungiyar sa finariti.
  • Bayan nan ne dai Tauraruwar Musa ta rika haskawa har ta kai Kungiyar CSKA Moscow su ka saye sa a 2012 bayan wasu da dama sun yi kokarin sayo ‘Dan wasan. Bayan shekaru kadan ne kuma ya koma Leicester City na Ingila.
  • A gida kuma dai Ahmed Musa ya nuna kwarewar a Super Eagles inda ya ci kwallo 2 a wasan Najeriya da Kasar Argentina a 2014. A Gasar cin kofin na Duniya da ake yi a bana ma dai Musa ya sake zura kwallaye 2.
  • Ahmed Musa dai ya auri Jamila wanda ta haifa masa ‘Ya ‘ya 2. Daga baya dai su ka rabu bayan sun samu sabani a Ingila. Musa ya koma ya auri Juliet Ejue wanda ta fito daga Kudancin Najeriya
  • Babban 'Dan wasan kwallon gaban na Kungiyar Leicester City Ahmed Musa dai mutum ne mai taimakon jama’a a Kano da ma Najeriya baki daya.
  • Ahmed Musa Musulmi ne wanda ya kuma rike addinin sa domin kuwa a kan gan shi a Masallaci da sauran wuraren ibada cikin kayan addini.
  • Babban 'Dan wasan ya taba rike Kyaftin din Super Eagles kuma shi yake goya lamba 7. Kafin nan Musa ya buga Kungiyar U-21 na Najeriya.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel