Alade mai nasibi da ya hango nasarar Trump a zaben Amurka, ya hangowa Najeriya nasara a gasar cin kofin Duniya

Alade mai nasibi da ya hango nasarar Trump a zaben Amurka, ya hangowa Najeriya nasara a gasar cin kofin Duniya

Masoya kungiyar kwallon kafa ta Najeriya sun cika da murna da farinciki bayan wani alade mai nasibi day a hango nasarar shugaba Trump gabanin zaben kasar Amurka, ya zabi kasashen Najeriya da Argentina nasarar zuwa zagayen kusa da na karshe a gasar cin kofin Duniya na kwallon kafa da za a fara bugawa a kasar Rasha.

Kazalika ya zabi kasashen Belgium da Uruguay a matsayin wasu kasashen da zasu fafata a zagayen kusa da na karshe.

Aladen da ake kira Mystic Marcus na da baiwar sansano duk inda nasara take da hancin sa kuma ya zuwa yanzu bai taba yin kuskure a hango nasara ba.

Alade mai nasibi da ya hango nasarar Trump a zaben Amurka, ya hangowa Najeriya nasara a gasar cin kofin Duniya
Alade mai nasibi yayin zaben kasashen da zasu yi nasara

Mai Aladen, Juliette Stevens, ya bayyana cewar Aladen sa bai taba yin hasashe an samu sabani ba domin ko a gasar cin kofin duniya ta shekarar 2014 saida ya hangowa kasar Spain nasara tun kafin a fara gasar.

DUBA WANNAN: An kama wani mutum da ya shiga Ka'aba da man fetur (Bidiyo}

Wasu abubuwan ban mamaki da aladen ya yi sun hada da has ashen ficewar kasar Ingila daga kungiyar kasashen turai da kuma nasarar shugaba trump a zaben kasar Amurka, a lokacinn da jama’a tuni suka bashi faduwa.

Alade mai nasibi da ya hango nasarar Trump a zaben Amurka, ya hangowa Najeriya nasara a gasar cin kofin Duniya
Alade mai nasibi da ya hango nasarar Trump a zaben Amurka, ya hangowa Najeriya nasara a gasar cin kofin Duniya

Yanzu abin jira a gani, shine ko hancin Aladen dake sansano nasara ya sansano daidai ko akasin haka a yayin da za a fara buga gasar cin kofin Duniyar ranar juma’a a kasar Rasha.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel