Kasar China za ta taimakawa Najeriya wajen samar da isassun gidaje

Kasar China za ta taimakawa Najeriya wajen samar da isassun gidaje

- Gwamnatin Buhari na kokarin samar da isassun gidaje a Najeriya

- Kasashe irin su China za su taimaka wajen ganin an ci ma hakan

- Wani kamfani a Kasar yayi alkawarin sa kudin sa a aikin da za ayi

Kasar Sin watau China ta nuna cewa a shirye ta ke da ta narka kudin ta wajen gine-ginen gidajen da za ayi a Najeriya domin ganin an rage matsalar da ake fama da shi na karancin gidajen zama.

Kasar China za ta taimakawa Najeriya wajen samar da isassun gidaje
Babatunde Fashola wanda shi ne Ministan gidaje na Najeriya

Mun samu labari daga Jaridar All Africa a karshen makon can cewa Kamfanin One Belt One Road da ke Kasar ta China za ta shiga cikin aikin gina gidaje a Kasar da za ayi. Shugaban wannan Kamfani Jin Changsheng yayi alkawarin hakan.

Mista Jin Changsheng ya bayyana wannan ne a wani taro da aka shirya kwanaki a Abuja. Mutanen kasar ta Chona sun fi shekaru 30 su na harkar gine-gine don haka sun kware kuma za su taimakawa wajen rage karancin gidajen da ake fama da su.

KU KARANTA: PDP ta fadawa Shugaban kasa Buhari ya daina yaudarar kan sa

An shirya taron domin kokarin jawo hankalin ‘Yan kasuwa da magina zuwa Najeriya inda ake kokarin gina gidaje 3000 a Birnin Tarayyan Abuja. Gwamnatin Tarayya na kokarin samawa kananan Ma’aikata da ‘yan tsaka-tsakiya gidaje ne a Najeriya.

Kwanakin Legit.ng ta rahoto cewa Gwamnatin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari za ta gina gidaje na sama da Naira Biliyan 1.3 a Jihar Sokoto.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel