Mun ga amfanin Gwamnatin Buhari Inji Gwamna Ikpeazu

Mun ga amfanin Gwamnatin Buhari Inji Gwamna Ikpeazu

- Gwamnan Jihar Abia ya bayyana cewa sun ga aikin Gwamnatin Buhari

- Okezie Ikpeazu yace a duk rana sai an ba ‘Yan makaranta a Jihar abinci

- Gwamnan yace an yi wata-da-watanni ana samun wutar lantarki a Abia

Mun ji labari daga Fadar Shugaban kasa cewa Gwamnan Jihar Abia ya yabawa Gwamnatin Shugaban kasa Muhammadu Buhari a dalilin wasu kokari da Gwamnatin ta ke yi na inganta harkar kasuwanci da kuma ilmin zamani.

Mun ga amfanin Gwamnatin Buhari Inji Gwamna Ikpeazu
Gwamna Okezie Ikpeazu yace Gwamnatin Buhari tayi masu kokari

A makon nan ne Mataimakin Shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ya kai ziyara Jihar Abia domin kaddamar da wasu ayyukan Gwamna Okezie Ikpeazu a bangaren kiwon lafiya. Bayan nan Yemi Osinbajo ya wuce Jihar Anambra.

KU KARANTA: Abaribe ya jefa Majalisa cikin hatsaniya da ya soki Buhari

A wajen taron, Gwamna Okezie Ikpeazu ya bayyana cewa Yaran makarantan Firamare a Jihar Abia na samun abinci kyauta a duk rana ta Allah. Gwamnan ya kuma ce an yi kusan watanni 5 kenan ba a dauke wuta ba wasu barayin.

Gwamnatin APC ta kawo wasu tsare-tsare na taimakawa marasa galihu a fadin Najeriya wanda daga ciki akwai ba ‘Daliban makaranta abin karin-kumallo. A jiyan ne dai kuma wani Sanatan na Abia ya soki Gwamnatin Shugaba Buhari.

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel