Da dumi-dumi: Yan bindiga sun kai farmaki ofishin yan sanda a jihar Kogi, sun hallaka hafsoshi 2

Da dumi-dumi: Yan bindiga sun kai farmaki ofishin yan sanda a jihar Kogi, sun hallaka hafsoshi 2

A yau Talata, 3 ga watan Afrilu wasu yan bindiga dadi sun far wa ofishin yan sanda da ke kauyen Gegu, hanyar Lokoja zuwa Abuja inda suka halaka yan sanda 2 da ke bakin aiki.

Kakakin hukumar yan sandan jihar, William Aya, ya bayyanawa manema labarai cewa yan bindigan sun jikkata wani fursuna da ke tsare a ofishin kuma an kaishi asibiti.

Ya ce an gabatar da gawawwakin jami’an yan sandan dakin ajiye gawawwakin asibitin Federal Medical Centre, Lokoja.

Da dumi-dumi: Yan bindiga sun kai farmaki ofishin yan sanda a jihar Kogi, sun hallaka hafsoshi 2
Da dumi-dumi: Yan bindiga sun kai farmaki ofishin yan sanda a jihar Kogi, sun hallaka hafsoshi 2

Mr Aya ya ce an kaddamar da bincike cikin al’amarin da ya faru misalin karfe 2 na dare.

A bangare guda, wasu jama’an garin sun bayyanawa manema labarai cewa kimanin yan bindiga 5 ne suka zo a kan babur.

Daga zuwansu suka budewa ofishin yan sandan wuta inda suka kashe yan sanda 2 a take.

KU KARANTA: Hukumar sojin Najeriya ta tura dakarun soji na musamman jihar Zamfara

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa ko a http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.ng Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel