Gwamnatin Rwanda ta haramta kiran Sallah a masallatai

Gwamnatin Rwanda ta haramta kiran Sallah a masallatai

- Birnin Kigali, babban virnin Rwanda yai kowanne birni kyau a Afirka

- Gwamnatin kasar ta haramta coci da masallatai saboda suna damun muutane yayin bacci ko hutawa

- A kasashe da dama ana samun karuwar wuraren ibada musamman masallatai ta coci-coci

Gwamnatin Rwanda ta haramta kiran Sallah a masallatai
Gwamnatin Rwanda ta haramta kiran Sallah a masallatai

A wani mataki da ka iya jawowa gwamnatin kasar bakin jini, an haramtawa masallatai a kasar Rwanda kiraye-kirayen sallah a lasifika, inda gwamnatin ta kira lamarin da bata iska, watau Noise Pollution wai don mutane na cewa an dame su.

Matakin na zuwa ne bayan da aka rushe akalla coci 700 a fadin babban birnin kasar, inda shugaban kasar Paul Kagame yace yana mamakin yadda suka basu a kasar kuma basu baiwa jama'ar kasar koda ruwan burtsatsai.

DUBA WANNAN: Zamu dawo da yan matan Dapchi, Buhari ya fadi a Yobe

Kungiyoyin addinai dai sunyi alla-wadai da matakin da karamar kasar ta tsakiyar Afirka ta dauka inda suka ce matakan na tauye hakkin jama'a na bin addinan da suke so.

A 1994, kasar ta Rwanda ta tsunduma yakin basasa inda taga kisan gilla na kabilanci wanda ya salwantar da akalla 800,000 daga kananan kabilun kasar (Tutsi) wanda manyan kabilu kasar suka shirya, (watau Hutu).

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng