Fursunoni 150 sun haddace Al-Qur’ani mai girma a gidan yarin Gombe

Fursunoni 150 sun haddace Al-Qur’ani mai girma a gidan yarin Gombe

Sashen musulman gidan yarin Gombe tare da gudunmuwar majalisar koli ta Musulunci shiyar jihar Gombe sun shirya gasar musabakan Al-Qur’ani domin murnan fursunoni 150 da suka haddace Al-Qurani mai girma.

A jawabin gwamnan jihar, Ibrahim Dankwambo, ya yabawa hukumar fursunonin Najeriya da wadanda suka shirya taron.

Kwantrolan gidan yarin ya yi kiraga sashen mabiya addinin Kirista suyi kokari wajen irin wannan abu da Musulmai sukayi wajen canza rayuwan Fursunoni.

KU KARANTA: Maryam Sanda ta mayar da martani a kan yamadidi da batun yiwa 'yar ta biki

Fursunonin sun samu kyautan kyaututtuka daban-daban daga hannun jama’a da kungiyoyi. An gudanar da was an kwaikwayo kan yadda fursunoni kan iya zama wajen ilimantar da al’umma.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel