Harin da aka kai wani Masallacin garin Mubi da safiyar nan ya rutsa da rayuka da dama

Harin da aka kai wani Masallacin garin Mubi da safiyar nan ya rutsa da rayuka da dama

- Wani matashi dan kunar bakin wake ya tayar da bam a wani masallaci dake garin Mubi, jihar Adamawa a safiyar yau

- Al’amarin ya afku ne da misalign karfe 5:20 na asuba, bayan sallar asuba; an rahoto cewa mutane 30 sun rasa rayukansu

- Kakakin yan sandan jihar Adamawa ya tabbatar da al’amarin inda ya bayyana cewa wadanda suka ji rauni na asibitoci daban-daban inda suke karban kulawa

Wani tashin bam ya afku a wani Masallaci dake garin Mubi, jihar Adamawa, a safiyar yau, Litinin, 21 ga watan Nuwamba, jaridar Punch ta ruwaito.

An rahoto cewa al’amarin ya afku ne a Kunu Araha, wani yanki na Arewacin Mubi, da misalin karfe 5:20 na safe.

Harin da aka kai wani Masallacin garin Mubi da safiyar nan ya rutsa da rayuka da dama
Harin da aka kai wani Masallacin garin Mubi da safiyar nan ya rutsa da rayuka da dama

Legit.ng ta tattaro cewa akalla sama da mutane 30 ne suka rasa rayukansu a bam din da matashi dan kunar bakin wake ya tayar.

KU KARANTA KUMA:

Kakakin yan sandan jihar Adamawa, Othman Abubakar ya tabbatar da afkuwar al’amarin.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel