Sabon rikici ya barke a jam'iyyar APC ta jihar Taraba

Sabon rikici ya barke a jam'iyyar APC ta jihar Taraba

Yanzu haka labaran da muke samu daga majiyoyin mu daban daban na nuni da cewa sabon rikici ya sake barkewa a jam’iyar adawa ta APC dake a jihar Taraba dai dai lokacin da tsohon mukaddashin gwamnan jihar Garba Umar ya koma jam’iyar.

Barkewar rikicin kuma ke da wuya sai wasu daga cikin kusoshin jam’iyar ta APC a jihar suka balle suka kuma kafa wata sabuwar abun da suka kira 'tafiya' da kuma suka kira kansu kungiyar yan 'integrity' watau gaskiya da rikon amana.

Sabon rikici ya barke a jam'iyyar APC ta jihar Taraba
Sabon rikici ya barke a jam'iyyar APC ta jihar Taraba

Legit.ng dai ta samu cewa su dai wadanda suka balle din sun hada da tsoffin Sanatoci da tsohon shugaban jam’iyar a jihar da yan wasu Majalisu da kuma masu ruwa da tsaki a siyasar jihar da dama inda kuma suka ce sun kafa wannan sabuwar tafiyar ne domin su ceto jam’iyar daga halin ha’ulai da suka ce wasu sun jefa ta a ciki.

To sai dai kuma a wani kakkausan martanin da dayan bangaren na jam'iyar ya maida, wanda ke zaman shugaban riko na jam’iyar a jihar, Alhaji Sani Chul da dama can yana tare da ministar harkokin mata da walwalar jama’a Aisha Jummai Alhassan, ya musanta zargin cewa basa tafiya da kowa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags:
APC