Sabon rikici ya barke a jam'iyyar APC ta jihar Taraba
Yanzu haka labaran da muke samu daga majiyoyin mu daban daban na nuni da cewa sabon rikici ya sake barkewa a jam’iyar adawa ta APC dake a jihar Taraba dai dai lokacin da tsohon mukaddashin gwamnan jihar Garba Umar ya koma jam’iyar.
Barkewar rikicin kuma ke da wuya sai wasu daga cikin kusoshin jam’iyar ta APC a jihar suka balle suka kuma kafa wata sabuwar abun da suka kira 'tafiya' da kuma suka kira kansu kungiyar yan 'integrity' watau gaskiya da rikon amana.
![Sabon rikici ya barke a jam'iyyar APC ta jihar Taraba Sabon rikici ya barke a jam'iyyar APC ta jihar Taraba](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt16f63u2uobog.jpeg?v=1)
Legit.ng dai ta samu cewa su dai wadanda suka balle din sun hada da tsoffin Sanatoci da tsohon shugaban jam’iyar a jihar da yan wasu Majalisu da kuma masu ruwa da tsaki a siyasar jihar da dama inda kuma suka ce sun kafa wannan sabuwar tafiyar ne domin su ceto jam’iyar daga halin ha’ulai da suka ce wasu sun jefa ta a ciki.
To sai dai kuma a wani kakkausan martanin da dayan bangaren na jam'iyar ya maida, wanda ke zaman shugaban riko na jam’iyar a jihar, Alhaji Sani Chul da dama can yana tare da ministar harkokin mata da walwalar jama’a Aisha Jummai Alhassan, ya musanta zargin cewa basa tafiya da kowa.
Asali: Legit.ng