Kasar Saudiyya na bukatar dabbobi 120,000 duk sati daga Najeriya

Kasar Saudiyya na bukatar dabbobi 120,000 duk sati daga Najeriya

- Kasar Saudiyya na bukatar dabbobi 120,000 duk sati daga Najeriya

- Gwamnan banki ya bayyana yadda za a kulla harkallar kasuwanci da wasu kasashen waje

- Ga duk mahajjati wajibi ne ya yanka dabba a kasar Saudiyya yayin aikin hajji

Gwamnan babban bankin kasa, Godwin Emefiele, ya bayyana hakan a yayin da yake gabatar da lakca a kan kalubalen masassar tattalin arziki da ribar da za a iya girba daga hakan, yayin da ya halarci taron lauyoyi na kasa a Legas.

Kasar Saudiyya na bukatar dabbobi 120,000 duk sati daga Najeriya
Kasar Saudiyya na bukatar dabbobi 120,000 duk sati daga Najeriya

Emefiele, ya bayyana cewar yanzu haka akwai yawaitar kasashe da ke kokarin kulla harkallar kasuwanci da Najeriya.

Emefiele, yace 'a misali, akwai bukatar naman halal daga kasashen larabawa da dama. A takaice muna da sahihin bayani cewar kasar Saudiyya zata bukaci kan dabbobi 120,000 duk sati.'

DUBA WANNAN: Duba Tsabar Kudin Da Gwamnatin Saudiyya Ta Biya ga Alhazan Da Aka Ciwa Mutunci

Kasar Saudiyya ce a farko cikin jerin kasashen duniya da ke sayen dabbobi daga kasashen ketare. Kasashen Sudan da Somalia ne ke samar wa Saudiyya mafi yawan dabbobin da take bukata. A shekarar 2016 kasar ta Saudiyya ta bawa kasar Zambiya kwangilar samar da awakai miliyan 1 duk wata.

A duk shekara miliyoyin jama'a ke halartar aikin hajji a kasar Saudiyya, kuma wajibi ne ga duk mai aikin hajji ya sayi tare da yanka dabba a kasar.

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng