Ministan Ilmi Adamu Adamu ya shiga uku

Ministan Ilmi Adamu Adamu ya shiga uku

- Adamu Adamu ya saba rubutu game da yajin aikin ASUU

- Yanzu haka Malaman Jami'a sun shiga yajin aiki

- Akwai dai aiki wur-jan-jan a gaban Ministan

Yanzu haka Ministan Ilmi A. Adamu ya shiga tsaka mai wuya a game da yajin aikin da Malama Jamia'a su ka shiga.

Ministan Ilmi Adamu Adamu ya shiga uku
Ministan Ilmi Mallam Adamu Adamu

Yanzu dai haka Kungiyar ASUU ta shiga yajin aikin da sai inna-ta-gani kuma Malam Adamu Adamu ne Ministan ilmi na kasar. Kowa dai yanzu ya zura idanu ya ga yadda za a kare. Wani Malamin Jami'ar Ahmadu Bello ta Zariya Kabiru D. Lawanti dai yace 'Yan siyasa duk saya su ke.

KU KARANTA: Gwamnati ta gargadi Yan Neja-Delta

Ministan Ilmi Adamu Adamu ya shiga uku
Kungiyar ASUU za ta yi yaji

A lokacin da Ministan Ilmi na yanzu Mallam Adamu Adamu yana rubutu a jarida ya saba sukar Gwamnati a duk lokacin da Malaman Jamia'a su ka shiga yajin aiki irin haka.

Tun kwanaki kamar yadda mu ka samu labari da dama na Malaman Jami'a sun zabi a tafi yajin aikin da sai inna ta gani saboda rashin jituwa tsakanin su da Gwamnati. Shirin yajin aiki ya kawo dar-dar a wajen masu karatu a halin yanzu.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Matasa su na fushi da kama masu garkuwa da jama'a

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng

Tags: