Dandalin Kannywood: Duk wadda ta ba da kanta don a sa ta fim laifin ta ne - Jaruma

Dandalin Kannywood: Duk wadda ta ba da kanta don a sa ta fim laifin ta ne - Jaruma

Wata sabuwar fuska a cikin jarumai mata na masana'antar finafinan Hausa mai suna Khadija Abubakar Mahmood ta bayyana cewa duk macen da ta bada kanta don a sata a cikin fim laifin ta ne.

Jarumar tayi wannan kalami ne a cikin wata fira da tayi da mujallar nan ta 'fim' wadda take kowo labaran fina finan Hausa lokacin da take amsa tambayar da ake yi mata game da maidu'in.

Dandalin Kannywood: Duk wadda ta ba da kanta don a sa ta fim laifin ta ne - Jaruma
Dandalin Kannywood: Duk wadda ta ba da kanta don a sa ta fim laifin ta ne - Jaruma

Legit.ng ta samu labarin cewa dai jarumar ta kuma bayyana cewa ita babu wanda ya taba kusantar ta da irin wannan zancen yayin da kuma take fadan cewa wasu matan su ke bada kofar a yi masu hakan.

Haka ma dai jarumar a cikin firar ta bayyana wasu daga cikin fina finan da ta taba fitowa a cikin su da suka hada da Gidauniya, Sahun Baya, Uwar Miji da dai sauran su.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng