YANZU YANZU: Jirgin sojin saman Najeriya ya fadi a ciki ruwa

YANZU YANZU: Jirgin sojin saman Najeriya ya fadi a ciki ruwa

- Jirgin sojin saman Najeriya ya fadi a cikin ruwa

- Baá san ainahin gurin da jirgin ya fada ba a arewa maso gabas

- Babu wanda ya rasa ransa a jirgin

- An kafa kwamitin bincike domin gano inda jirgin ya ke

Wani jirgi mai saukar ungulu Augusta 106 mallakar rundunar sojin saman Najeriya ya hadu da sharrin karfe, sannan ya fada a cikin ruwa wanda baá gano ko ina bane a arewa maso gabas.

Daraktan hulda da jamaá kuma jami’in bayana na hukumar sojin sama, Air Commore Olatokunbo Adesanya, wanda ya tabbatar da faruwar alámarin a ranar Alhamis, yace baá rasa rayuka ba, ya kara da cewa matukin jirgin ne ya sanya jirgin a ruwa domin rage ‘barna.

Majiyarmu ta ce ana nan ana kokari a yanzu domin gano inda jirgin yake.

YANZU YANZU: Jirgin sojin saman Najeriya ya fadi a ciki ruwa
Jirgin sojin saman Najeriya ya fadi a ciki ruwa

“A take Shugaban rundunar ya hada kwamitin bincike domin su gano ainahin abun day a haddasa alámarin.

KU KARANTA KUMA: Matsin tattalin arziki rahama ne ga Najeriya – OyegunMatsin tattalin arziki rahama ne ga Najeriya – Oyegun

“Tuni mambobin kwamitin sun isa Maiduguri domin fara aiki,” Inji Adesanya.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng