Kalli yadda wani malamin musulunci ya daure dalibinsa da mari (HOTUNA)
Hotuna sun billon a wani karamin yaro wanda aka ce malamin islamiyar su ne ya daura masa mari a jihar Kaduna.
Legit.ng ta gano cewa wata mai amfani da shafin Facebook Aishat Alubankudi ta yada hotunan wani dalibi a jihar Kaduna wanda aka rahoto cewa malamin Islamiyyar su mai suna Mallam Sufi ya daura masa mari. Ta yi kira ga wgwamnan jihar Kaduna Mallam Nasir El-Rufai da ya taimaka ya ceci yaron.
KU KARANTA KUMA: Mulkin farar hula ake yi a Najeriya ba dimokradiyya ba - Tinubu
A cewar ta: “Gwamna Mallam Nasir El-Rufai dan Allah ayi bincike. Wannan rahoto da ba’a tabbatar ba! An tura wannan yaron makarantar Islamiyya a Zaria daga kauyen Boko dake jihar Zamfara.
![Kalli yadda wani malamin musulunci ya daure dalibinsa da mari (HOTUNA) Kalli yadda wani malamin musulunci ya daure dalibinsa da mari (HOTUNA)](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkytqlagjrdujn8.jpeg?v=1)
“Malamin sa ya daure sa da mari sannan kuma ya tura sa yin bara na abincin da zai ci. Sunan Mallamin Sufi, a yankin Rimin Tsiwa dake birnin Zariya jihar Kaduna. Makaranatar Islamiyyar na jikin gidan Alhaji Sani Rimin Tsiwa.
![Kalli yadda wani malamin musulunci ya daure dalibinsa da mari (HOTUNA) Kalli yadda wani malamin musulunci ya daure dalibinsa da mari (HOTUNA)](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt2j293i375i3.jpeg?v=1)
“Wannan na daga cikin tsarin Almajiranci. Babu mamaki yaron ya ji wuya ne sai ya yi yunkurin guduwa don haka ya daura masa mari a lokacin da ya kama shi."
Legit.ng zata sanar da ku halin da yaron ke ciki da zaran an kuma bayar da bayani.
Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa
Ko a http://twitter.com/naijcomhausa
Asali: Legit.ng