Masari azzalumin mutum ne – Ibrahim Shema

Masari azzalumin mutum ne – Ibrahim Shema

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema yayi watsi da rahoton wata kwamitin bincike sa gwamnan jihar, Aminu Bello Masari, ya nada domin binciken gwamnatinsa.

Ya bayyana wannan ne ta mai magana da yawunsa, Oluwabusola Olawale.

Yace: “Abin damuwa ne kuma ba dadin ji ace wata kwamitin bincike sa gwamna Aminu Masari ya nada zatayi watsi da hukuncin kotun daukaka kara da kuma kotun koli sannan ta fara wani aikin sa kai da gwamna Masari ya sata wanda ke nuna zalunci, kama karya, da amfani da kujera wajen sabawa dokar da umurnin kotu.

“Saboda haka muna watsi da wata barazana, rashin adalci, saba doka, da rashin girmama doka kuma ba zamu amince da sakamakon wannan rahoto na zalunci ba.”

Masari azzalumin mutum ne – Ibrahim Shema
Masari azzalumin mutum ne – Ibrahim Shema

Olawale ya nanata cewa kotun daukaka kara ta dakatad da kwamitin saboda Masari bai bi hanyar da ya kamata ba wajen zaben shugaban kwamitin.

KU KARANTA: Aisha Buhari ta dawo Najeriya daga Landan

Ya kira hankalin mutane ga wasikar da Masari ya rubutawa gwamnan jihar Flato, Simon Lalong, a 2016 inda Masari ke bukatan wani alkali ya jagoranci kwamitin.

https://twitter.com/naijcomhausa

https://web.facebook.com/naijcomhausa/?ref=bookmarks

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng