Dalilin da yasa luwadi ke karuwa a Najeriya – Gwamnatin tarayya

Dalilin da yasa luwadi ke karuwa a Najeriya – Gwamnatin tarayya

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa luwadi ta zama ruwan dare a Najeriya yayinda matasan Najeriya sun fara yinshi.

Dirakta Janar na hukumar NIA, Garba Abari, ya bayyana wannan ne a wani taron tattaunawa kan yaki da rashawa a Abuja ranan asabar.

“Wani abu mai muhimmanci da ya kamata in bayyana shine kallon tashohin kasashen waje na zama kalubale ga addinin mutanenmu da kuma al’adanmu. A yanzu ana yaudaran matasanmu da abubuwan da suka sabawa koyarwan addininmu da kuma al’adunmu.

Dalilin da yasa luwadi ke karuwa a Najeriya – Gwamnatin tarayya
Dalilin da yasa luwadi ke karuwa a Najeriya – Gwamnatin tarayya

“Zana hotuna a jiki wanda aka fi sani da ‘Tattoo’, askin yan iska, janye wando kasa da kuma penti a kai ya zama ruwan dare tsakanin matasanmu mata da maza.”

KU KARANTA: Sarauniyar kyau ta karbi Musulunci

“A yanzu matasanmu na bayani a fili cewa a hallata auren jinsi kuma suna shirin kai zanga-zangarsu majalisar dokokin tarraya domin neman da sunan hakkin dan Adam,”.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng