Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un: Allah yayiwa Alh Ahmadu Chanchangi rasuwa

Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un: Allah yayiwa Alh Ahmadu Chanchangi rasuwa

Wannan hamshakin maikudi haihuwa jihar Taraba, mazaunin jihar Kaduna, Alh Ahmadu Chanchangi ya rasu ne a hanyar Kaduna zuwa Abuja yayinda ake kokarin kaisa Abuja asibiti da safiyar yau Laraba.

Wata majiya ta bayyana cewa : “Ya rasune a hanya yayinda muke kokarin kaishi asibiti a Abuja, bayan wata rashin lafiya da yayi.”

Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un: Allah yayiwa Alh Ahmadu Chanchangi rasuwa
Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un: Allah yayiwa Alh Ahmadu Chanchangi rasuwa

Ya rasu ya bayar mata 3 da yara 33, daya daga cikinsu shine shugaban kwamitin kwasta na majalisan wakilan tarayya, Rufai Chanchangi.

KU KARANTA: Gwamnatin Kano ta bada izinin mayar da masallacin Idi Kasuwa

“Za’ayi jana’izara misalin karfe 1 na rana a gidansa da ke kwanan Chanchancgi Tudun wada Kaduna s kuma za’a kaishi makabartan Bashama Road.”

Daga cikin wadanda suka fara kai ta’ziyya shine mataimakin shugaban masu rinjayen majalisan dattawa, Bala Ibn NA Allah.

https://web.facebook.com/naijcomhausa/#

https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: