Shugaba Buhari ya jajintawa jami’ar Maiduguri

Shugaba Buhari ya jajintawa jami’ar Maiduguri

- A yau Najeriya ta waye gari cikin wani labara mai susan ciki na tashin Bam a jami’ar Maiduguri

- Ana sa ran mayakan Boko Haram ne suka kai wannan mumunan hari

Shugaba Buhari ya jajintawa jami’ar Maiduguri
Shugaba Buhari ya jajintawa jami’ar Maiduguri

Bam din ya tashi ne a cikin masallaci inda mutane 5 suka rasa rayukansu kuma wasu 20 sun jinkita. Shugaban sashen likitancin dabbobi na jami’ar, Farfesa Aliyu Mani, ya hallaka a hadarin.

Kana wata Bam din ta ske tashi a hanyar mashigar jami’ar inda mutane ke wucewa. Wannan abu ya tayar da hankalin mutane.

KU KARANTA: Kalli hotunan harin Bam da aka kai Jami'ar Maiduguri

Shugaba Muhammadu Buhari ya mika sakon jajenshi ne ta hanyar mai Magana da yawunsa Femi Adesina.

Yace: Shugaba Muhammadu Buhari yayi Allah wadai da harin da aka kai jami’ar Maidguri da safiyan ann. Shugaban kasan ya jajintawa jami’ar, gwamnatin jihar Borno, da iyalan wadanda suka rasa rayukansu da kuma mutanen jihar Borno.

Kana kuma yana gaishe da wadanda suka raunana ,yana tayasu addu’an sauki da kuma kwanciyan hankali ga iyalansu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng