Soyayya: Sabbin ma’aurata a sansanin yan gudun hijira sun samu tagomashi
A ranar Lahadi 8 ga watan Janairu ne jami’an hukumar bada agajin gaggawa (NEMA) suka daura ma wasu masoya aure a sansanin yan gudun hijira dake Yola, jihar Adamawa.
![Soyayya: sabbin ma’aurata a sansanin yan gudun hijira sun samu tagomashi Soyayya: sabbin ma’aurata a sansanin yan gudun hijira sun samu tagomashi](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt122d7dqedoog.jpeg?v=1)
Masoyan da aka fara daura ma aure sune Abdu Kanuma da amaryarsa Fanta Mohammed, yayin da na biyun kuwa sune Ango Baba Goni da Falta Babagoni a matsyain amaryarsa.
KU KARANTA:Kwanaki 1000 da sace yan matan Chibok: Buhari yayi alkawarin dawo dasu
Hukumar NEMA ta mika musu kyautana kayayyakin abinci da sauran kayayyakin amfani don su tabbatar da tsaftan jikkunansu.
![Soyayya: sabbin ma’aurata a sansanin yan gudun hijira sun samu tagomashi Soyayya: sabbin ma’aurata a sansanin yan gudun hijira sun samu tagomashi](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt7kc1bmhf1fe.jpeg?v=1)
Cikin kyautukan da suka samu sun hada da kwalayen taliyar Indomie, man shampoo, madara, ruwan roba, sabulun wanka da sauransu.
Allah ya basu zaman lafiya
Ku cigaba neman labaran mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa ko a http://twitter.com/naijcomhausa
Asali: Legit.ng