Zahra Buhari tayi tsadaddan taron wankan Amarya

Zahra Buhari tayi tsadaddan taron wankan Amarya

- Zahra Buhari ta kusa kasancewa amaryan dan biloniya Ahmed Indimi

- Kyakkyawar yar ta shugaban kasa zata shiga jerin daya daga cikin mafi kyawun taron da ya faru a Disamba 2016

- Don daraja taron, ta yi wani hadadden taron wankan amarya a filin liyafa na fadar shugaban kasa a jiya, 13 ga watan Disamba.

Zahra Buhari tayi tsadaddan taron wankan Amarya
Zahra Buhari tayi tsadaddan taron wankan Amarya

Zahra ta kasance jakadiya mai kwazon aiki na kungiyar Ace charity, wani kungiyar sadaqa da aka kafa ta don rage yaduwar cutar sikila a fadin kasar. Kyakkyawar yar shugaban kasa ta nuna ma duniya tausayinta, yanzu lokaci yayi da zata shiga kan hanyar ma’aurata.

Don girmamawa ga aurenta da dan biloniya Ahmed Indimi wanda aka shirya yi a ranar 16 ga watan Disamba, ta hada kykkyawan liyafa na wankan amarya a filin liyafar fadar shugaban kasa a jiya, 13 ga watan Disamba.

Mai shirin zama amaryan ta fito cikin tsantsar kyawu kuma anyi taron cikin lafiya kamar yadda muke tabbatar da burin bikin da kansa ya kasance.

KU KARANTA KUMA: Buhari ya gabatar wa majalisa kasafin kudin 2017

Kalli hotunan wankan amaryan a kasa:

Zahra Buhari tayi tsadaddan taron wankan Amarya
Zahra Buhari tayi kyau a taron wankan Amarya
Zahra Buhari tayi tsadaddan taron wankan Amarya
Zahra Buhari tayi tsadaddan taron wankan Amarya
Zahra Buhari tayi tsadaddan taron wankan Amarya
Yanda aka shirya gurin taron wankan Amarya na Zahra Buhari

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng